Shekaru 10 da rashin ka Sarkin Gwoza Shehu Mustapha Idriss Timta

Baba Ina mai gaya maka.
Published from Blogger Prime Android App
Tun da ka tafi ka bar mu a haka. 
Babu cigaba kuma babu haɓaka.
Sun kashe Sir Isa Dan uwan ka
Sun rakarkata maka garin ka 
Sun keta haddin muradun ka 
Sun kona duk wani makarantun ka 
Sun daina daraja iyalan gidan ka 
Kulluma kunci harda kuka 
An daina yin noma a garin ka 
Mutanen ka sun koma maroka
An maida su yawo kamar hauka 
Zuciya ta rube kamar tauka 
Babu wani babba da zai tuna ka 

Magana nake kamar waka 
Mai tunani kadai zai san haka 
Gaskia nake amman fahimtar ka 
Roko nake, ka tsaya a haka
Me suke da shi da zan roka
Bayan ni dasu akwai doka 
Kar ka tsaya bata lokacin ka 
Gaskia ɗaci take ina gaya maka 

Me suke da shi da zasu baka 
Bayan kai dasu kun wuce haka 
Sun dade suna satar kudin ka 
Sun kasa yi maka abin cigaban ka 
Babu wakilci da zai nuna ka 
Kunya zaka ji idan anyi haka 

Da su nake ƴan siyar ka 
Ka rike su kamar Allahn ka 
Tunani kake su daukaka 
Bayan ma daga kai suke samun daukaka
Babu kai babu su ka shaida haka 
Da ka, ka, ka, nake sauke haka
Magana nake saɓanin fahimtar ka 
In ka gane ya ishe ka haka 
In kuma ka kiya ku shaida haka 

Allah yayi rahama ya kuma jikan ka
Gaskia daya ce, mun rasa ka